Ɗan bindiga a Colorado ya kashe mutum shida saboda ‘ba su gayyace shi liyafa ba’

Family members mourn together

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Ƴan uwan waɗanda aka kashe su shida a wani bikin zagayowar shekarar haihuwa na jimamin lamarin a wani gidan tafi da gdanka da ke Colorado Springs, Colorado

Jami’an gwamnati a jihar Colorado sun sanar da cewa wani mutum dauke da bindiga ya kashe mutum shida yayin wata liyafar zagayowar shekarar haihuwa da aka yi a karshen mako saboda ba a gayyace shi ba.

‘Yan sanda sun ce Teodoro Macias mai shekara 28 ya harbe budurwarsa Sandra Ibarra-Perez mai shekara 28 da ‘yan uwanta biyar kafin daga baya ya harbe kansa da kansa da bindigar da ya ke dauke da ita.

Wannan lamarin ya auku ne a wani gidan tafi da gidanka da ke Colorado Springs da sanyin safiyar Lahadi.

Bikin an shirya shi ne domin wasu ‘yan uwan budurwar su uku, amma uku cikinsu sun rasa rayukansu a harin.

Wannan harin ya auku ne kasa da wata biyu bayan wani harin irin wannan da aak yi a wani shago da ke birnin Boulder na jihar ta Colorado wanda ya yi sandiyyar mutuwar muum 11.

Yan sanda sun kuma ce ɗan bindigan na fama da matsalar “mallakar abin da yake ƙauna”, kuma an san shi da tsananin kishi.

Ranar Talata ƴan sanda sun bayyana sunayen sauran mutum biyar da su ka rasa rayukansu a harin, kowanne da shekarunsa na haihuwa:

  • Melvin Perez, 30
  • Joana Cruz, 53 (Melvin’s mother)
  • Jose Gutierrez Cruz, 21 (Melvin’s brother)
  • Mayra Perez, 32 (Melvin’s wife)
  • Jose Ibarra (Mayra’s brother)

Yan sanda sun ce bai yi rajistar bindigar da ya aikata wannan aika-aikar ba.

(BBC Hausa)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...