Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Wani Fitaccen Ɗan Kasuwa Tare Da Yin Garkuwa Da Ƴarsa Da Matarsa A Jihar Katsina

Ƴan fashin daji  sun kai farmaki ƙauyen Mairuwa dake ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina ranar Asabar da daddare dai-dai lokacin da ake gudanar da Sallar Tarawih.

A kalla mutane biyu aka harbe s har lahira a yayin da mutum guda kuma ya jikkata.

Ɗaya daga cikin mutanen da aka kashe, Alhaji Lado fitaccen ɗan siyasa ne kuma babban manomi ne a garin.

Wata majiya dake garin ta ce an kashe marigayin ne bayan da ya nuna turjiya lokacin da ƴan fashin dajin suke ƙoƙarin tafiya da shi.

Wani mutum da ya tsira daga harin ya ce ƴan bindigar sun samu nasarar yin garkuwa da mata da kuma biyu daga cikin ƴaƴan marigayin.

Mutum na biyu da aka kashe a harin wani ma’aikacin lafiya ne da yake aiki a Cibiyar Kula Da Lafiya ta Mairuwa.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...