Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban jami’a  a Benue

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da wasu ɗalibai mata na jami’ar Joseph Sarwuan Tarka dake Makurdi babban birnin jihar Benue.

Ɗaliban da yawansu ya kai huɗu anyi garkuwa da su da maraicen ranar Talata a ginin jami’ar na North Core Campus.

Wata majiya ta ce ɗaliban sun tafi aji ne domin yin karatun dare lokacin da aka yi garkuwar da su.

Ƴan bindigar sun farma bangaren otal na jami’ar kafin su yi awon gaba da ɗaliban.

Mintoci kaɗan bayan faruwar dakarun rundunar sojan Najeriya sun isa makarantar.

Sewuese Aneneh mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar ta faɗawa jaridar The Cable cewa labarin da  ya same su ya nuna cewa dalibai biyu ne kawai aka yi garkuwa da su.

Aneneh ta ƙara da cewa tuni rundunar ƴan sanda ta kaddamar da bincike kan faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]