Ƴan bindiga sun sace ƴan mata 6 a jihar Neja

Ƴan mata shida dake da shekaru 15 zuwa 17 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun yi garkuwa da su a garin Pandogari dake ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Neja.

Mazauna gari sun faɗawa jaridar Daily Trust cewa ƴan fashin dajin sun farma garin da tsakar daren ranar Laraba inda suka kashe wani ɗan bijilante Aliyu Aminu tare da yin garkuwa da ƴan matan..

Ƴan fashin dajin masu yawa  sun shiga garin ne daga wajejen  ɓangaren Birnin Gwari ta wajen Kwalejin Fasaha ta Mamman Kantagora dake Pandogari.

Wata majiya ta bayyana cewa ƴan matan da aka yi garkuwa da su an ɗauke su zuwa Dajin Kwangel.

Ɗaya daga cikin majiyar ta bayyana cewa ƴan fashin dajin sun riƙa bi gida-gida a lokacin harin.

Shugaban ƙaramar hukumar Rafi, Ayuba Usman Katako ya tabbatar ya tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da ya yi da gidan rediyon Prestige FM.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]