Ƴan Bindiga Sun Kashe Ɗan Sanda Ɗaya Tare  Kubutar Ɗaurarru  7 Daga Wani Gidan Yari A Jihar Imo

Aƙalla  ɗaurarru 7 dake gidan yarin Okigwe a jihar Imo suka tsere daga gidan yari a wani hari da ƴan bindiga suka kai a ranar Litinin.

A wata sanarwa da aka fitar bayan kai harin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar,Henry Okoye ya ce maharan sun kuma kashe insifectan ɗan sanda.

Okoye ya ce kwamishinan yan sandan jihar,Aboki Danjuma ya tura rundunar kar ta kwana da za ta bi sawun maharan.

Ya ƙara da cewa ana zargin yan bindigar mambobi ne na ƙungiyar ƴan ta’addar IPOB dake fafutukar kafa ƙasar Biafra.

Jihar Imo dai ta kasance jihar dake gaba-gaba a yankin kudu maso gabas dake fama da tashin hankalin mayaƙan ƙungiyar ta IPOB.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...