Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da jakar da ta bata mai dauke da sama da Naira miliyan 100.

A ƙarshen taron wa’azi na musamman da aka gudanar a Bauchi, Daraktan kungiyar Agaji ta farko na kasa Engr Mustapha Imam Sitti ya yabawa Kankia bisa gaskiyarsa.

Kungiyar JIBWIS reshen jihar Bauchi ta bayyana a shafinta na sada zumunta na Facebook cewa Kankia ya gano jakar kuma ba tare da bata lokaci ba ya kai rahoto ga ‘yan sanda. 

Mai shi ya tabbatar da cewa babu abin da ya ɓace a cikin kuɗin.

Bisa la’akari da gaskiyarsa, kungiyar Izala ta karrama Kankia da lambar yabo da kuma daukar nauyinsa a  aikin hajjin bana.

Ya kuma karbi Naira miliyan biyu daga hannun Hon.  Abdulmalik Zannan Bangudu da motar bas daga Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed domin fara harkar kasuwanci.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...