Za mu yi da’a ga kotu a kan Sowore – Malami | BBC Hausa

Khad MuhammedLawHausa6 years ago

Latsa hoton da ke sama don kallon cikakken bidiyon

Ministan shari’ar Najeriya Abubakar Malami ya ce gwamnatin kasar za ta yi da’a ga umarnin kotun kasar a kan sakin dan siyasa kuma dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore, wanda yake hannun hukumomin kasar.

A farkon makon nan wata babbar kotun tarayya a Abuja da ke Najeriya ta bai wa hukumar tsaro ta farin kaya DSS umarnin sakin mawallafin jaridar Sahara Reporters ta intanet Omoyele Sowore.

Sai dai a yayin yanke hukuncin, kotun ta umarci Sowore ya bayar da fasfonsa na tafiye-tafiye.

Hakan na zawa ne bayan da DSS ta janye karar da ta kai babbar kotun tarayyar wanda ta nemi a ci gaba da tsare Omoyele Sowore kan zargin hannu a ta’addanci.

Leave a reply

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...