Za mu yi da’a ga kotu a kan Sowore – Malami | BBC Hausa

Latsa hoton da ke sama don kallon cikakken bidiyon

Ministan shari’ar Najeriya Abubakar Malami ya ce gwamnatin kasar za ta yi da’a ga umarnin kotun kasar a kan sakin dan siyasa kuma dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore, wanda yake hannun hukumomin kasar.

A farkon makon nan wata babbar kotun tarayya a Abuja da ke Najeriya ta bai wa hukumar tsaro ta farin kaya DSS umarnin sakin mawallafin jaridar Sahara Reporters ta intanet Omoyele Sowore.

Sai dai a yayin yanke hukuncin, kotun ta umarci Sowore ya bayar da fasfonsa na tafiye-tafiye.

Hakan na zawa ne bayan da DSS ta janye karar da ta kai babbar kotun tarayyar wanda ta nemi a ci gaba da tsare Omoyele Sowore kan zargin hannu a ta’addanci.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...