Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi – AREWA News

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya – NAN, ya ruwaito mai Magana da yawun hukumar gidan yari a jihar Abubakar Adamu, yana cewa lamarin ya auku ne a jiya Juma’a, sakamakon wani jami’i da ya shiga da wasu kayayyaki ga fursunoni a haramce.

“An sami hatsaniya ne sakamakon halayyar wani jami’in hukumar gidajen yari, da ke shigar da wayyoyin salula da miyagun kwayoyi wa fursunoni da ke gidan yarin,” in ji Abubakar Adamu.

Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi
Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi

Ya ce fada ne ya soma tashi tsakanin fursunonin da aka shigarwa da kayayyakin a haramce, da kuma jami’an da ke kokarin hana aukuwar ayukan da suka saba ka’ida a gidan yarin.

Abubakar ya kara cewa “an yi sa’ar ganin jami’in dumu-dumu yana aikata wannan haramtaccen aikin aka kuma kama shi, abin da ke nan ya bakanta ran fursunonin da aka shigar wa da kayayyakin, suka ta da bore har suka fasa dakunan ajiye kayayyaki, suka kwashe shebura da digogi da sauransu.”

Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi
Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi

Daga nan ne fa fusatattun fursunonin suka soma rera wakoki da take, inda suka ci gaba da farfasa gine-gine da kayayyaki a cikin gidan yarin, lamarin da kuma ya tilastawa jami’an hukumar soma harbi a iska domin razanasu, wanda kuma yayi sanadiyyar fursunoni 5 da jami’ai 2 suka ji rauni, a cewar kamfanin dillancin labaran na NAN.

To sai dai Abubakar Adamu ya ce tuni da aka sami shawo kan matsalar, yayin da kuma dukkan fursunoni suka koma dakunansu.

Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi
Yunkurin Fasa Gidan Yari A Bauchi

Rahotanni sun bayyana cewa an tsaurara matakan tsaro tare kuma da takaita zirga-zirgar ababen hawa a kewayen gidan yarin, kana kuma aka sanya shingaye akan dukkan titunan da ke zuwa gidan yarin.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...