Hukumar majalisar dinkin duniya mai kula da ‘yan gudun hijira ta fitar da wani rahoto inda ta bayyana cewa cikin yara ‘yan gudun hijira miliyan daya da dubu dari bakwai na duniya, rabinsu ba su samun ilimin boko.
Ta bayar da dalilai da suka hada da bukatar bayar da muhimmanci ga kare lafiyar yara sama da ba su ilimi, da kuma gazawar da iyayen yara ke yi na kasa biyan kudin makaranta.
Hukumar ta ce damar da yara ‘yan gudun hijira ke da ita na samun ilimin sakandare na dada raguwa yayin da suke kara girma.
Hukumar ta yi kira ga gwamnatoci da kuma makarantu da kamfanoni masu zaman kansu da zuba jari wajen fito da kyakyawan shiri da zai tabbatar yaran sun samu rayuwa mai inganci.
Ko a kwanakin baya sai da Majalisar wakilai a Amurka ta amince da wani kudurin doka inda za a samar da dala miliyan hudu da dubu dari shida domin tallafawa masu fama da matsi da kuma fatara da ke kan iyakar kasar.
Shi ma Fafaroma Francis a kwanakin baya ya bayar da tallafin dalar Amurka dubu 500 ga ‘yan gudun hijira.
Dama hukumar hukumar amjalisar dinkin duniya mai kula da ‘yan gudun hijirar ta bayyana cewa yawan mutanen da tashin hankali ya raba da muhallansu ya wuce miliyan 70, adadi mafi girma da aka taba gani a tarihi.