Ƙungiyar Yan Uwa Musulmi ta Najeriya wato shi’a ta bayyana cewa mambobin kungiyar 1000 ne suka bace bayan artabun da suka yi da jami’an tsaro a birnin tarayya Abuja.
Mambobin sun shafe kwanaki uku suna zanga-zanga a birnin tarayya Abuja duk da cewa sojoji da Æ´ansanda sun gargade su kan yin haka.
A yayin zanga-zangar ne aka kashe wasu daga cikinsu wasu da dama suka samu raunuka ya yin da aka kama mutane 400.
A wata sanarwa ranar Laraba, Abdullahi Musa mai magana da yawun kungiyar ya ce kari kan mutane 1000 da suka bace an kashe 46 ya yin da mutane 107 suka jikkata.
Ƙungiyar ta ci alwashin cigaba da zanga-zangar neman a saki shugaban su, Sheikh Ibrahim Elzakzaky ba tare da gindaya wasu sharuda ba.