Yan sanda sun kwato shanu 36 daga hannu barayin shanu a Zamfara – AREWA News

Rundunar yan sandan jihar Kebbi, ta karbo shanu 36 daga hannun barayin shanu a jihar Zamfara a cewar kwamishinan yan sandan jihar,Garba Danjuma.

Danjuma ya fadawa manema labarai ranar Lahadi a birnin Kebbi cewa wasu daga cikin barayin an kama su tare da shanun ya yin da wasu suka tsere.

“Jami’an mu masu bincike sun tafi daga Birnin Kebbi zuwa Zamfara domin karbo shanun bayan da wasu mutane biyu, Abubakar Juli da Alhaji Ardo daga kauyen Asarara sun kai rahoton sace shanu 43 ranar 10 ga watan Satumba.

“Bayan cikakken bincike ma’aikatan mu sun kama, Abubakar Umar da Attahiru Sani daga kauyen Daki Takwas a karamar hukumar Gummi ta jihar Zamfara bayan da aka same su da mallakar shanu 36 na sata,”

“Sauran mutanen da ake zargi da satar shanu sun samu nasarar tserewa amma muna bin sawunsu kuma nan ha dadewa ba zamu kama su,” ya ce.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar ƙera bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...