
Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu fitattun mutane biyu da ake nema ruwa a jallo bisa zargin aikata fashi da makami a sassa daban-daban na jihar.
Mutanen da aka kama sun hada da Kabiru Isah da Monday Bulus. Jami’an sashen yaki da fashi da makami na rundunar ne suka cafke su a ranar 10 ga Janairu, 2026, bayan samun sahihin bayanan sirri.
Kakakin rundunar, SP Ramhan Nansel, ya ce an kama mutanen ne a yankin Azuba Centre da ke Lafia, inda ake zargin sun je shirya wani sabon aikin laifi. Ya bayyana cewa tuni jami’an tsaro suka sanya su cikin kulawa ta musamman kafin a kama su.
A yayin kamen, ’yan sanda sun kwato bindigar G3 guda daya ba tare da lambar tantancewa ba daga hannun wadanda ake zargin. Daga bisani, a ranar Lahadi 11 ga Janairu, 2026, an kuma sake kwato wata bindigar pump-action a wani samame na daban.
SP Nansel ya ce kamen mutanen ya samo asali ne daga aikin ’yan sanda na amfani da bayanan sirri wajen yaki da laifi.