Wasu ‘yan Najeriya uku Abubakar Muhammad da Amir Yunus Goro da kuma Abdulganiyyi Amin sun yi nasarar lashe kyautuka a gasar karatun Al Kur’ani ta 2019 a kasar Saudiyya a matakai daba-daban.
Gwani Idris Abubakar Muhammad daga jihar Borno ta Najeriya, ya zo na daya ne a ajin farko na izu sittin ba tare da tafsiri ba.
Wannan nasara da ya samu ta ba shi damar lashe kyautar riyal na Saudiyya 120,000 – kimanin kusan naira milyan ₦12,000,000.
Sai Amir Yunus, wanda shi kuma ya zo na uku a ajin farko na izu sittin da tafsiri, inda ya samu kyautar riyal 150.000 – sama da naira miliyan ₦14,000,000.
Abdulganiyyi Amin shi ne na ukun, wanda ya zo na uku shi ma a aji na biyu na izu sittin ba tare da tafsiri ba.
Shi kuma ya samu kyautar riyal 40,000 – kusan naira miliyan ₦4,000,000.