‘Yan Najeriya biyar sun riga mu gidan gaskiya a wajen aikin Hajji

Kamar yadda a ka sanar tun farko, tawagar alhazan Najeriya ta karshe ta sauka a Jeddah bayan tashi daga filin saukar jiragen sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja.

Rukunin na karshe na cikin adadin alhazan jihohi dubu 44,450 banda maniyyatan dake tafiya ta jirgin yawo.

Hukumar alhazan ta bayyana cewa a dauki matakan ganin cewa mahajjata sun sami kular da ya kamata ta wajen ajiye jami’in hukuma a dukan wuraren da aka sauke mahajjata. Aka kuma kara jan hankalin masu aikin hajin su kula bayan samun labarin wadansu suna kokarin damfarar alhazan da suka fahimci cewa, suna bukatar taimako. Ta dalilin haka suka takaita shigowar baki masaukan alhazai a Makkah da Madina don lamuran tsaro.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...