‘Yan ciranin da suka makale sun bar wani tsibirin Italiya

stranded

Kusan ‘yan cirani 100 da ke kan wani jirgin ruwa na jin kai wanda ya makale a tsibirin Lampedusa sun bar tsibirin na Italiya, bayan wani mai shigar da kara ya umarci jirgin ruwan da ya bar tsibirin.

Lokacin da jirgin ya isa tsibirin dai, mutane sun yi musu maraba a yayin da suka dinga sowar “sannu da zuwa” musamman ma ga ‘yan ciranin Afirka.

Mai shigar da kara, Luigi Patronaggio ya umarci da a kwace jirgin wanda mallakin wata kungiyar agaji mai suna Open Arms ne.

Kungiyar ta ce ‘yan ci ranin za su iya fara samun kulawar likitoci, duk da gwamnatin Italiya ta jima tana hana su shiga kasar.

Kafin mai shigar da karar ya yanke hukuncinsa, Sipaniya wadda ita ce gida ga kungiyar ta Open Arms ta aika wani jirgin ruwa zuwa Lampedusa domin ya dauko ‘yan ci ranin.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...