Yan bindiga sun sace ɗaliban firamare 6 a jihar Nasarawa

Yan bindiga sun sace yara 6 a firamaren LEA dake Alwaza a ƙaramar hukumar Doma ta jihar Nasarawa.

Rahotanni sun bayyana cewa yan bindigar sun sace yaran ne da misalin ƙarfe 07:00 na safe.

Rahman Nansel kakakin rundunar yan sandan jihar Nasarawa shi ne ya tabbatar wa da jaridar The Cable faruwar lamarin.

Nansel ya kara da cewa tuni aka bincike tare kokarin ceto yaran.

Jihar Nasarawa dai na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya dake fama da matsalolin tsaro.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...