Wasu yan bindiga a ranar Litinin sun kai farmaki kauyen Kikuba dake Gundumar Chawai a karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna inda suka cinnawa gidaje 21 wuta dake yankin.
Yan bindigar sun isa Yankin suna harbin kan me uwa da wabi da misalin karfe 06:30 na yammacin ranar Litinin a cewar hakimin yankin Yahaya Muhammad.
Jaridar ta gano cewa kauyen na da makotaka da jihar Plateau.
Hakimin na Chawai wanda ya kasance a garin Kaduna domin ganawa da kwamishinan Ć´ansandan jihar shine ya bayyana wa jaridar Daily Trust abin da ya faru a wata tattaunawa.
Ya ce yan bindigar sun kuma kai farmaki kauyen unguwar Rimi inda suka kashe wasu samari uku a ranar da suka kai hari kauyen Kikuba.
“Sun kai farmaki Kikuba da misalin karfe 06:00 na yamma ranar Litinin a garin dake iyakar Kaduna da Plateau. Kauyen na karkashin Gundumar Chawai akalla gidaje 21 aka kone ya yin da mutum guda ya rasa ransa a harin.