Yan bindiga sun kona gidaje 21 a wani ƙauye dake Kaduna

Wasu yan bindiga a ranar Litinin sun kai farmaki kauyen Kikuba dake Gundumar Chawai a karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna inda suka cinnawa gidaje 21 wuta dake yankin.

Yan bindigar sun isa Yankin suna harbin kan me uwa da wabi da misalin karfe 06:30 na yammacin ranar Litinin a cewar hakimin yankin Yahaya Muhammad.

Jaridar ta gano cewa kauyen na da makotaka da jihar Plateau.

Hakimin na Chawai wanda ya kasance a garin Kaduna domin ganawa da kwamishinan ƴansandan jihar shine ya bayyana wa jaridar Daily Trust abin da ya faru a wata tattaunawa.

Ya ce yan bindigar sun kuma kai farmaki kauyen unguwar Rimi inda suka kashe wasu samari uku a ranar da suka kai hari kauyen Kikuba.

“Sun kai farmaki Kikuba da misalin karfe 06:00 na yamma ranar Litinin a garin dake iyakar Kaduna da Plateau. Kauyen na karkashin Gundumar Chawai akalla gidaje 21 aka kone ya yin da mutum guda ya rasa ransa a harin.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]