Yan bindiga sun kona gidaje 21 a wani ƙauye dake Kaduna

Wasu yan bindiga a ranar Litinin sun kai farmaki kauyen Kikuba dake Gundumar Chawai a karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna inda suka cinnawa gidaje 21 wuta dake yankin.

Yan bindigar sun isa Yankin suna harbin kan me uwa da wabi da misalin karfe 06:30 na yammacin ranar Litinin a cewar hakimin yankin Yahaya Muhammad.

Jaridar ta gano cewa kauyen na da makotaka da jihar Plateau.

Hakimin na Chawai wanda ya kasance a garin Kaduna domin ganawa da kwamishinan ƴansandan jihar shine ya bayyana wa jaridar Daily Trust abin da ya faru a wata tattaunawa.

Ya ce yan bindigar sun kuma kai farmaki kauyen unguwar Rimi inda suka kashe wasu samari uku a ranar da suka kai hari kauyen Kikuba.

“Sun kai farmaki Kikuba da misalin karfe 06:00 na yamma ranar Litinin a garin dake iyakar Kaduna da Plateau. Kauyen na karkashin Gundumar Chawai akalla gidaje 21 aka kone ya yin da mutum guda ya rasa ransa a harin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]