Yan bindiga sun kashe jami’an kwastam biyu a jihar Kebbi

Wasu yan bindiga da ake zargin mayakan Lakurawa ne sun kashe jami’an hukumar kwastam biyu yan bindiga suka kashe a  garin Tugar dake ƙaramar hukumar Bagudo ta jihar Kebbi.

Jaridar The Punch ta rawaito cewa yan bindigar sun farma wani shingen binciken jami’an da tsakar daren ranar Laraba.

Wata majiya ta bayyana cewa an kone daya daga cikin jami’an kurmus bayan da yan bindigar suka cinna wuta ɗakin da yake kwance yana bacci.

” Yan bindigar sun kai farmaki kan shingen binciken jami’an guda biyu dake kusa da juna.Sun harbe wani karamin jami’i guda ɗaya a yayin da suka ƙone babban jami’i ɗaya  da ransa,” a cewar majiyar.

” Sun zo a cikin motar ɗaukar kaya inda suka batar da kama a zuwan sun ɗauko dabbobi hakan ya sa sun shammaci jami’an. Har ila yau kwantar da Jami’ai biyu a asibiti da suka samu raunin harbin bindiga,”

More from this stream

Recomended