Rundunar sojin Chadi ta ce ta kashe mayakan Boko Haram 1,000 a wani samame da ta kai yankin Tafkin Chadi.
Kakakin rundunar sojin Kanar Azem Agouna ya ce an kashe dakarun Chadi 52 a bata-kashin da aka kwashe kwana shida ana yi a tsakaninsu.
Shugaba Idriss Déby ya ziyarci yankin Tafkin na Chadi. Ya ce babu dan kungiyar Boko Haram ko daya da ya rage a yankin.
Ya yi takaici kan yadda ya ce an bar Chadi ita kadai take fatattakar mayakan na Boko Haram a fadin Tafkin na Chadi, wanda ke da iyaka da kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.
An kaddamar da farmakin ne bayan da a watan jiya sun kashe dakarun Chadi kusan 100 a harin da suka kai musu a yankin.
Har yanzu dai babu wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da ikirarin sojojin Chadin kuma Boko Haram bata ce komai ba.