Mutum 13 ne suka rasa rayukansu wasu 10 kuma suka ji raunuka a wani hatsarin mota da ya faru a kan hanyar Legas zuwa Ibadan a ranar Laraba.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa abin ya faru ne a Saapade kusa da garin Ogere, kamar yadda Clement Oladele kwamandan hukumar kiyaye hadura mai kula da shiyya a jihar Ogun ya tabbatar.
Mista Oladele ya ce hatsarin ya auku ne da misalin karfe 5:00 na yamma a Saapade, inda kamfanin RCC mai aikin gyaran titin ya karkatar da hanya saboda aikin.
Ya ce wata motar daukar kaya ce ta haddasa shi bayan tayarta ta fashe yayin da take tsaka da gudu a kan hanyarta zuwa Legas daga Ibadan.
“A saboda haka ne motar ta afka wa wasu motocin guda biyu da suke nufar Ibadan bisa yunkurin da daya daga cikinsu ta yi na yanke dayar a daidai inda aka samu sauyin hanya,” in ji shi.
Ya kara da cewa motoci uku ne abin ya rutsa da su.