Wolverhampton ta gano barakar Man City | BBC Sport

Man City

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester City ta yi rashin nasara a hannun Wolverhampton da ci 2-0 a wasan mako na takwas da suka fafata a gasar Premier ranar Lahadi a Ettihad.

Wannan ne karon farko da Wolverhampton ta ci Manchester City a babban wasan tamaula tun bayan 1979.

Kuma Wolverhampron ta ci kwallon farko ta hannun Adama Traore saura minti 10 a tashi daga wasan, kuma shi ne ya kara na biyu daf da za a tashi daga karawar.

Kawo yanzu City ta barar da maki biyar a gida a wasa hudu a bana, bayan da a bara uku ta rasa a kakar da ta lashe kofin Premier.

Kawo yanzu Liverpool wadda take ta daya a kan teburin Premier ta bai wa City wadda take ta biyu tazarar maki takwas a kakar bana.

City ta buga 2-2 da Tottenham a Ettihad a wasannin bana, haka kuma ta yi rashin nasara a hannun Norwich City da ci 3-2 a gasar ta Premier.

Wolverhampton tana mataki na 12 a kan tebrurin Premier da maki 10.

Manchester City za ta ziyarci Crystal Palace a wasan mako na tara a gasar ta Premier ranar 19 ga watan Oktoba.

Ita kuwa Wolverhampton za ta karbi bakuncin Southampton a wasan mako na tara ranar ta 19 ga watan Oktoba.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...