Wata mata a jihar Kebbi ta cakawa mijinta wuka ya mutu

Wata matar aure mai suna Hafsat Sani ta cakawa mijinta, Muhammad Garba dan shekara 30 wuka a karamar hukumar Suru dake jihar Kebbi.

Matar auren yar shekara 25 da marigayi mijin nata sun samu sabani har ta kai su ga cacar baki a gidansu dake kauyen Tundifari a karamar hukumar ta Suru inda ta dauki wuka ta caka masa a cibiya.

Da yake tabbatarwa da yan jaridu faruwar lamarin ranar Litinin , kwamishinan yansandan jihar,Garba Muhammad Danjuma ya ce an kama Hafsat ya yin da kuma ake cigaba da bincike.

Ya ce lamarin ya faru ne ranar 25 ga watan Maris 2019.

Kwamishinan ya kuma tabbatar da kama wasu mutane da suka kashe wata matar aure Bilkisu Zayyanu da kuma yarta mai shekaru uku mai suna Hadiza Zayyanu a yankin Dolekaina dake Kamba.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...