Wata matar aure mai suna Hafsat Sani ta cakawa mijinta, Muhammad Garba dan shekara 30 wuka a karamar hukumar Suru dake jihar Kebbi.
Matar auren yar shekara 25 da marigayi mijin nata sun samu sabani har ta kai su ga cacar baki a gidansu dake kauyen Tundifari a karamar hukumar ta Suru inda ta dauki wuka ta caka masa a cibiya.
Da yake tabbatarwa da yan jaridu faruwar lamarin ranar Litinin , kwamishinan yansandan jihar,Garba Muhammad Danjuma ya ce an kama Hafsat ya yin da kuma ake cigaba da bincike.
Ya ce lamarin ya faru ne ranar 25 ga watan Maris 2019.
Kwamishinan ya kuma tabbatar da kama wasu mutane da suka kashe wata matar aure Bilkisu Zayyanu da kuma yarta mai shekaru uku mai suna Hadiza Zayyanu a yankin Dolekaina dake Kamba.