Wata mata a jihar Kebbi ta cakawa mijinta wuka ya mutu

Wata matar aure mai suna Hafsat Sani ta cakawa mijinta, Muhammad Garba dan shekara 30 wuka a karamar hukumar Suru dake jihar Kebbi.

Matar auren yar shekara 25 da marigayi mijin nata sun samu sabani har ta kai su ga cacar baki a gidansu dake kauyen Tundifari a karamar hukumar ta Suru inda ta dauki wuka ta caka masa a cibiya.

Da yake tabbatarwa da yan jaridu faruwar lamarin ranar Litinin , kwamishinan yansandan jihar,Garba Muhammad Danjuma ya ce an kama Hafsat ya yin da kuma ake cigaba da bincike.

Ya ce lamarin ya faru ne ranar 25 ga watan Maris 2019.

Kwamishinan ya kuma tabbatar da kama wasu mutane da suka kashe wata matar aure Bilkisu Zayyanu da kuma yarta mai shekaru uku mai suna Hadiza Zayyanu a yankin Dolekaina dake Kamba.

More News

Rundunar Sojan Najeriya Ta Fitar Da Sunayen Sojojin Da Aka Kashe A Jihar Delta

Rundunar sojan Najeriya ta fitar da hoto da kuma sunayen sojoji 16 da aka yiwa kisan gilla a jihar Delta. Ranar Alhamis ne aka kashe...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...

Wasu ƴan mata a Najeriya sun ƙirƙiro janareta mai amfani da fitsarin mutum

Wasu matasa ‘yan Najeriya hudu sun kirkiro wani janareta mai amfani da litar fitsari don samar da wutar lantarki ta sa’o’i shida. Ƴan matan –...