Wasu Masu Garkuwa Da Mutane Sun Mika Wuya

VOA Hausa

Tubabbun mutanen, wadanda ba a bayyana sunayensu ba sun kuma ba da hadin kai kan cewa za su taimaka wajen magance wannan matsala ta garkuwa da mutane da ta zama ruwan dare a yankin.

Daya daga cikinsu ya sheda wa wakilin VOA Ibrahim Abdulaziz cewa, “muna kama mutane ne don mu samu kudi, kuma yadda muke samun kudin a banza haka kudin ke karewa a banza.”

Ya kuma yi kashedi ga tsoffin abokanan huldar tasa.

“Duk mutanen da suka san suna aikin garkuwa da mutane har yanzu, wadanda na yi aiki da su a baya, idan ba su kawo kansu ba, to ni zan mika su ga hukuma,” a cewarsa.

'Yan sandan jihar Adamawa, da makaman da aka kwace hannun masu garkuwa da mutanen.
‘Yan sandan jihar Adamawa, da makaman da aka kwace hannun masu garkuwa da mutanen.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Audu Madaki, ya ce a yanzu suna samun ci gaba sosai wajen gudanar da ayyukansu.

Ya kara da cewa, suna kai samame cikin yankunan da masu garkuwa da mutanen ke boye wa domin hana su zama a yankunan.

“Ta hakan muke samun hana su gudanar da wadannan miyagun ayyukan, lamarin da ke janyo su kawo kansu wurinmu domin mu taimaka masu da sana’o’in da za su iya yi,” inji kwamishinan.

Ya kara da cewa, “mun kafa masu sansanonin da za su dinga aiki da ‘yan kungiyar Miyetti Allah, sannan muna karbar bayanai na tsoffin abokan aikinsu masu garkuwa da mutane domin mu kama su.”

A lokuta da dama, akan zargi al’umar Fulani da hannu dumu-dumu a harkar satar mutane a sassan Najeriya.

Shugaban kungiyar Miyetti Allah Alhaji Ja’oji Isa a jihar ta Adamawa, ya ce za su ci gaba da ba da hadin kai domin a kawo zaman lafiya a jihar.

Wannan nasarar ta biyo bayan kiran da manyan sarakunan jihar suka yi tare da hadin gwiwar kungiyoyin Fulani irinsu Miyetti Allah, na cewa, za’a gudanar da addu’o’in tsinuwa wato Puulaku, ga duk wani bafillace da ke da hannu a ayyukan garkuwa da jama’a.

Hakan duk na faruwa ne kwanaki kadan bayan da aka gudanar da adu’o’in zaman lafiya a jihar, bisa matsalar tsaro da ake yawan fuskanta.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...