Tsohon ministan harkokin waje na Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen shekarar 2027.
Tuggar ya gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa damar da ya ba shi na yin aiki a matsayin minista, yana mai cewa hakan ya ƙara masa fahimtar yadda ake gudanar da mulki tare da shirya shi don yi wa al’ummar Bauchi hidima.
Ya ce ya sauka daga mukaminsa na gwamnati domin bin ƙa’idojin da suka shafi masu rike da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara.
A cewarsa, manufarsa ba ta kashin kai ba ce, illa inganta rayuwar al’ummar jihar, inda ya nuna damuwa kan talauci da ƙarancin ingantaccen ilimi da kiwon lafiya.
Tuggar ya bayyana cewa gogewarsa a harkokin kasuwanci da noma za ta taimaka masa wajen fahimtar matsalolin manoma da makiyaya. Ya kuma yi alƙawarin mayar da hankali kan bunƙasa noma, samar da hanyoyin karkara, da ƙarfafa tattalin arziki.
Dangane da tsaro, ya ce zai ɗauki matakan ƙarfafa tsaron al’umma ta hanyar haɗin gwiwa da shugabannin gargajiya da kuma tattaunawa domin kawo zaman lafiya.
Ya ƙara da cewa zai tabbatar manoma, ‘yan kasuwa da ɗalibai sun gudanar da ayyukansu cikin aminci ba tare da tsoro ba.
Tuggar Ya Bayyana Aniyar Tsayawa Takarar Gwamnan Bauchi A 2027

