Tsokacin masana game da kalaman Buhari a taron ministoci

Fadar shugaban Najeriya ta shirya taron sanin makamar aiki ga sabbin ministoci da shugaban ya nada domin gudanar da gwamnati a zango na biyu.

Yanzu haka masu fashin baki a fannin siyasar Najeriya na tsokaci game da kalaman da shugaban kasar ya yi a lokacin da ya gabatar da jawabi a wurin taron sanin makamar aikin ga asabbin ministocin da ya nada.

Batutuwan da shugaban na Najeriya ya tabo, a wurin taron, sun hada da bitar nasarorin zangon farko na gwamnatinsa da kalubalen yawan jama’a da Najeriya ke fuskanta da mafarkin gwamnatinsa na aza tubalin fitar da matalauta miliyan 100 daga kangin fatara cikin shekaru 10 masu zuwa.

Shugaban ya kuma tabo batun bukatar da ke akwai ga sabbin ministocin su hada hannu wuri guda ta fuskar tsarawa da aiwatar da manufofin cimma burin gwamnati a ma’aikatun da za su jagoranta.

Sai dai masu kula da lamura sun yi tsokaci game da lafuzzan shugaban.

Kwamared Kabiru Sa’idu Dakata, shugaban kungiyar CAJA masu rajin tabbatar da adalci kawar da rashawa da kuma alkinta dukiyar kasa, ya ce bayannan shugaban sun saka shakku a zukatan jama’ar kasar.

Ya kuma kara da cewa jawabin nasa ya nuna cewa ita gwamnati ba ta da shirin da za ta kai kasar ga inda ta ce za ta kai ta.

Shi ma masanin kimiyyar siyasa da harkokin dimokaradiya, ya yi tafsili game da kalaman na shugaba Buhari.

Malam Kabiru Sufi, malami ne a kwalejin share fagen shiga Jami’a ta Kano, ya kuma ce jama’a suna jiran su ga an fitar da wani daftari ko wani babban kudiri da ya wuce wanda aka fitar a halin yanzu.

Yanzu dai ‘yan Najeriya na dakon ganin kamun ludayin sabbin ministocin bayan shugaba Buhari ya tura su ma’aikatun da za su yi wani lokaci a nan gaba.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...