Tsare El-zakzaky : IMN ta mayar wa El-Rufa’i martani | BBC News

Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption

Kotu ta ba da umarnin sakin El-Zakzaky tun a shekarar 2016 amma a na ci gaba da tsare shi

A Najeriya, ‘yan kungiyar harkar Musulunci, ta mazhabar Shi’a, wato Islamic Movement of Nigeria, ta mayar da martani ga gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i,

Wannan na zuwa bayan da ta zargi gwamnan da yin kalaman cewa Shugaban kungiyar Sheikh Ibrahim Elzakzaky ba zai taba fita daga gidan yari ba matsawar yana mulkin jahar.

A cewar Ibrahim Musa shugaban dandalin yada labarai na kungiyar a Najeriya, El-Rufa’i ya yi kalamin ne a hira da wani gidan rediyo a ranar Juma’a.

Ibrahim Musa ya ce ga alama gwamnan yana da wani dalili na kashin kansa na ci gaba da tsare jagoransu Sheikh Ibrahim El-Zakzaky.

Ya kuma ‘kara da cewa kotu ta ba da umarnin sakin El-Zakzaky tun a shekarar 2016 amma gwamnati ta ci gaba da tsare shi babu dalili.

Masu fafutukar kare hakkin dan adam na yawan sukar gwamnati kan ci gaba da tsare sheikh Ibrahim El-zakzaky, suna cewa gwamnatin ba ta mutunta umurnin kotu tana kuma karan tsaye ga dokokin kasar.

Rikici tsakanin ‘ya’yan ‘kungiyar da hukumomin tsaro a Najeriya ya yi sanadiyyar mutuwar daruruwan musamman yan ‘kungiyar ta IMN.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...