Tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Gaza ya samu cikas | BBC Hausa

Fireball

Hakkin mallakar hoto
AFP

Israila ta kaddamar da sabbin hare-hare kan mayakan Falasdinu bayan da aka samu sabbin hare-haren roka daga Gaza kwana daya bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Kafafen watsa labaran Falasdinawa sun ce makamai masu linzami sun fada kan wasu wurare mallakar kungiyar mayaka ta Palestinian Islamic Jihad (PIJ) da safiyar Juma’a, abin da ya janyo raunata mutum biyu.

Hakan dai na zuwa ne bayan harba wa Israi’la wasu makaman roka ranar Alhamis, bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyar PIJ ta ayyana.

Rikici tsakanin Israila da Falasdinawa dai ya kara rincabewa bayan da Israila ta kashe babban kwamandan kungiyar PIJ ranar Litinin.

Isra’ila ta ce Baha Abu al-Ata ‘hadari’ ne kasancewarsa mutumin da ya kitsa kai wa Israila harin roka na baya-bayan daga Gaza.

Fiye da rokoki 450 ne aka harba kan Israila, inda ita kuma ta kaddamar da hare-haren sama a kan Gaza a kwanaki biyu da suka kwashe suna fafatawa.

Hakkin mallakar hoto
AFP

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...