Tottenham: Sissoko zai yi jinya zuwa watan Afirilu

Tottenham

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Dan wasan Tottenham, Moussa Sissoko zai yi jinya zuwa watan Afirilu, bayan aiki da likitoci suka yi masa a gwiwar kafarsa.

Dan kwallon mai shekara 30, ya yi raunin ne a wasan da Tottenham ta yi rashin nasara a hannun Southampton da ci 1-0 a sabuwar shekarar 2020.

Dan wasan tawagar Faransa ya buga wa Tottenham wasa 20 daga 21 da ta yi a Premier bana, inda ya ci kwallo biyu a raga.

Tottenham ta ce za ta sa ido kan jinyar da zai yi, domin ya koma fagen fama a farkon watan na Afirilu.

A makon jiya ne Tottenham ta sanar Harry Kane zai yi jinya, koda yake ba a fayyace lokacin da zai koma buga kwallo ba.

Tottenham tana ta shida a kan teburin Premier League, maki biyar tsakaninta da Chelsea ta hudu a teburin.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...