Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da sarakuna biyu daga jihar Niger a fadar Aso Rock dake Abuja.
Shugaban kasar ya gana da Sarkin Borgu, Mohammed Halliru Dantoro da kuma takwaransa na Kontagora, Muhammad Barau.
Har ila yau Tinubu ya gana da tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari.
Tinubu ya kuma samu ganawa da shugaban kamfanin NNPCL, Mele Kyari da kuma, Samuel Ogbuku shugaban hukumar NDDC ta bunƙasa yankin Niger Delta.