Tawagar gwamnatin tarayya ta duba aikin titin Kano zuwa Abuja – AREWA News

Gani yadda aikin ginin hanyar Kano zuwa Abuja ke cigaba da tafiyar hawainiya yasa gwamnatin tarayya ta aike da wata tawaga ta musamman domin duba halin da ake ciki game da aikin.

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje shi ne ya tarbi yan tawagar a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano dake Kano.

Tawagar ta kunshi shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ministar kudi,Zainab Shamsuna Ahmad da kuma ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Fashola.

Tawagar ta duba yadda aikin yake tafiya tun daga Kano zuwa Kaduna inda acan ne za su gudanar da taron masu ruwa da tsaki kan aikin titin.

Mutane da dama dai sun dade suna kokawa kan yadda aikin yake tafiya duba da tsawon lokacin da aka dauka ba ayi wani aikin azo a gani.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...