Sunday Igboho: Dillalin motoci da ke korar Fulani daga kudancin Najeriya | BBC Hausa

Sunday Igboho

Yayin da magoya bayansa ke yi masa kirari, su kuwa masu adawa da shi na kallon a matsayin bakin-ganga kuma wani mutum mai haɗari da ke tayar da wutar ƙabilanci da kashe-kashe.

A shekarun baya, a yankinsu na kudu maso yammacin Najeriya kaÉ—ai aka san Sunday “Igboho” Adeyemo, amma yanzu ya zama É—aya daga cikin waÉ—anda aka fi tattaunawa a kansu – kuma masu raba kan al’umma – a faÉ—in Najeriya.

Cikin wasu kalaman rura wuta, mutumin da ke sana’ar sayar da motoci ya yi tsamo-tsamo a cikin rikicin Æ™abilanci – wato rikici tsakanin Fulani makiyaya da sauran Æ™abilu.

Rikici tsakanin manoma da makiyaya game da filayen noma da kuma burtali ya yi sanadiyyar kashe dubban mutane a cikin shekara 20 da suka gabata.

An kambama shi a wani fim

Bayan kashe wani É—an siyasa a watan da ya wuce, Mista Adeyemo ya ja hankalin duniya bayan ya buÆ™aci Fulani makiyaya ‘yan arewacin Najeriya su bar yankin kudu maso yamma, inda Yarabawa ke zaune, saboda zargin aikata laifuka.

Sai dai mutumin da ake tunanin yana kare masu rauni, Igboho – wanda ya samo sunansa daga garinsu a Jihar Oyo – ya daÉ—e yana jawo fitina.

An kambama É—an shekara 48 din a cikin wani fim da aka yi a shekarun 1990 da harshen Yarabanci, inda aka nuna rikici tsakanin wasu al’umma biyu. Haka nan fim É—in na cike da tsafe-tsafe da guraye da layu.

A cikin wata fitowa a fim ɗin a lokacin da wasu ƙabilu za su fafata, tauraron fim ɗin mai suna Adeyemo ya zo a kan babur sannan ya ɗauki wata ayaba mai guba kuma ya ci ba tare da wani abu ya same shi ba. Sai kawai ya fito da bindiga ya buɗe wa abokan gabarsa wuta.

Wannan fim É—in da ire-irensa – ciki har da wanda yake yawo da maciji a wuyansa – ya jawo ana yi masa kallon gagara-badau.

  • An haife shi a 1972 a Igboho da ke Jihar Oyo
  • Yana sana’ar sayar da motoci sabbi da kuma waÉ—anda aka yau
  • Makaniken babur ne lokacin da yake matashi
  • Yana da gidauniya mai sunansa da ke tallafa wa mabuÆ™ata

Adeyemo ya tayar da Æ™ura a Æ™asa baki É—aya a lokacin da ya yi amfani da ranar bikin ‘yancin kai a watan Oktoba ya yi kira da a Æ™irÆ™iri Æ™asar Yarabawa mai zaman kanta, duk da cewa mutane sun tsangwame shi game da shawarar tasa.

Yanzu da yake ƙara zama fitila ga magoya bayansa, an fara ɗaukar ƙorafe-ƙorafensa da mahimmanci.

Maganar mallakar ƙasa ce kan gaba a cikin ƙorafin da yake yi ɗin.

Bayanan hoto,
Sauyin yanayi na ƙara tilasta wa Fulani makiyaya yin nisan kiwo zuwa kudu domin ciyar da shanunsu

Fulani makiyaya tare da iyalansu kan yi tafiyar kilomita dubbai daga Arewa zuwa Kudu a Najeriya da ma wajen ƙasar aƙalla sau biyu a shekara domin kiwo. Sai dai hakan ya sha jawo rikici tsakaninsu da mutanen yankunan da suke bi, inda ake zarginsu da lalata amfanin gona.

Kazalika, ana zargin wasunsu da aikata garkuwa da mutane domin kuÉ—in fansa.

Wasu daga cikin masu arziki a Kudu kan É—auki Fulanin aiki domin kula musu da shanunsu da suke kiwo.

Wani yunÆ™uri da gwamnnatin Tarayya ta yi a 2019 domin kawo Æ™arshen matsalar ta hanyar Æ™irÆ™irar wuraren kiwo bai yi nasara ba, yayin da akasarin gwamnonin Kudu suka Æ™i amincewa da shi suna masu zargin Shugaba Buhari da Æ™oÆ™arin mallaka wa ‘yan Æ™abilarsa Æ™asa.

Rikicin ya Æ™ara Æ™amari a ‘yan shekarun nan sakamakon Fulanin da manoman suna É—aukar makamai domin kare kansu daga hare-haren da suke kai wa juna.

Kazalika, gwamnonin yankin na kudu maso yamma sun ƙirƙiri wata rundunar tsaro mai suna Amotekun domin su yaƙi matsalar.

Haka nan, an haramta yawon kiwo a dukkanin jiha shida na yankin.

Lamarin ya ƙara rincaɓewa a watan Disamba biyo bayan kisan wani ɗan siyasa a Jihar Oyo mai suna Fatai Aborode.

Adeyemo ya yanke shawarar É—aukar fansa ta hanyar korar Fulani ba tare da bayar da wata hujjar da ke nuna hannunsu a cikin laifin da kuma sauran kashe-kashen da ake aikatawa.

Bayan wa’adin da ya ba su na kwana bakwai ya cika a watan Janairu, ya jagoranci wani maci a yankin da aka yi kisan, inda aka Æ™ona gidajen wasu Fulani da suka shafe shekaru a wurin.

‘Jikina kyarma yake idan aka ambaci sunansa’

Abdulkadri Saliu, shi ne shugaban Fulani a yankin wanda aka ƙona gidansa kuma yanzu yake gudun hijira, ya zargi Adeyemo da kunna wutar rikici.

“Nakan ji tsoro duk sanda aka ambaci sunan Igboho,” in ji shi, yana mai cewa bai taÉ“a ganin tashin hankali kamar haka ba.

Ya ce an kashe ƙaninsa yayin harin.

Bayanan hoto,
Abdulkadri Saliu ya zargi Adeyemo da haddasa tashin hankalin da ya yi sanadiyyar ƙona gidajensu

Adeyemo ya musanta zargin da ake yi masa na haddasa tashin hankali, yana cewa ‘yan sandqa sun goya masa baya tun daga farko har Æ™ashen lamarin.

Amma fa ya yi tattaki zuwa Yewa na Jihar Ogun domin korar Fulanin daga can ma.

Wasu dandazon matasa ne suka tarÉ“e shi, inda ya riÆ™a ziga su da cewa “‘yan daba makiyaya” sun tsira da laifin da suka aikata saboda “saboda makiyaya na kusa da gwamnatin tarayya”.

“Duk wani Bafulatani da ke aikata garkuwa da mutane ya kamata a fito da shi,” a cewarsa.

‘Yan sanda sun ce suna bincike kan lamarin amma sun kasa tabbatarwa ko yana cikin waÉ—anda ake zargi da tayar da fitina.

Wani ɗan majalisar tarayya Shina Peller ya yabi Adeyemo cikin wani saƙo da ya wallafa a Instagram.

Sai dai wasu ‘yan siyasa daga arewacin Najeriya sun yi Allah-wadai da ayyukan nasa, suna zarginsa da haddasa Æ™abilanci da kuma fitar da ‘yan Æ™asa daga wuerin zamansu ba bisa doka ba.

Kazalika, wani asusu da aka buɗe mai suna GoFundMe domin tallafa wa ayyukan nasa ya samu naira miliyan 10 cikin ƙasa da kwana ɗaya.

‘Yan Najeriya na da ikon zama a duk inda suke so’

Masu goyon bayan Adeyemo na zargin gwamnatin tarayya da ƙin yin abin da ya kamata wurin dakatar da hare-haren makiyaya a kan mazauna ƙauyuka.

Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom, wanda kafin ‘yan kwanakin nan jiharsa ke kan gaba wurin irin wannan rikici, na ganin cewa lamarin ya ta’azzara ne saboda tausayin da shugaban Æ™asa ke nuna wa Fulani makiyaya.

Ministan YaÉ—a Labarai da Al’adu ya faÉ—a wa BBC cewa ba zai mayar da martani ba game da kalaman gwamnan, yana mai cewa “‘yan Najeriya na da ikon zama a kowane É“angare na Æ™asar”.

Shi ma shahararren marubucin nan É—an yankin kudu maso yamma, Wole Soyinka, ya soki Buhari kan shurun da ya yi game da ayyukan makiyayan.

“Me suke tsammani daga gare mu tun da yanzu yaÆ™i ya cim mana? Tabbas za a riÆ™a samun yunÆ™urin matasa wanda idan muka zauna jiran gwamnatin tarayya za mu zama bayi a garuruwanmu,” kamar yadda ya faÉ—a wa BBC.

Ya ce Adeyemo ya mayar da martani ne ta hanyar ya fi kwarewa a kai.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...