Sojojin Sun Kashe Ɗan Ƙungiyar ISWAP A Jihar Borno

Sojojin rundunar tsaro ta Operation Haɗin Kai da aka ajiye a Miringa sun samu nasarar kashe wani mayaƙin ƙungiyar ƴan ta’addar ISWAP lokacin da suka daƙile wani farmaki da aka kawo musu.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ranar 24 ga watan Faburairu inda gamayyar sojojin runduna ta 231 da 331 dake aiki a makarantar Command Science Girls Secondary School dake ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno suka fuskanci hare-hare daga wasu ƴan bindiga dake kan babura.

Sojojin sun yi nasarar daƙile harin har ta kai ga sun kashe mutum guda daga cikin ƴan ta’addar.

Sojojin sun gano bindiga ƙirar PKT da kuma harsashi da da dama.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...