Sojojin sun kama wani mai kai wa ƴan ta’adda kayan agaji

Rundunar sojin Operation Hadin Kai ta kama wani yaro ɗan shekara 15 da ake zargi da aikin kai kayan agaji da kuɗi ga mayakan ƙungiyar ISWAP a jihar Borno.

Wani rahoto ya bayyana cewa an kama yaron ne a garin Ngamdu yayin wani samame da sojoji suka gudanar a yankin Ngamdu–Benisheik.

Wata majiya mai bincike kan tsaro, Zagazola Makama, ta wallafa a shafinta na X cewa yaron da aka kama mai suna Tijjani, yana cikin waɗanda ake zargi da taimaka wa hare-haren da aka kai a Benisheik da Ngamdu.

A cewar rahoton, Tijjani ya amince a binciken farko cewa ya shiga cikin wasu hare-haren da aka kai a yankin, sannan ya bayyana cewa an tura shi da kuɗi Naira 850,000 domin siyan kayan amfani ga mayakan.

Ya kuma ce mayaƙan sun fito ne daga Jilli, wadda ake zargi da zama mafakar ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Gubio, kafin su kai hare-hare sannan su koma can.

Rahoton ya ƙara da cewa sojoji na ci gaba da bincike domin gano sauran waɗanda ke cikin wannan rukunin da kuma yanke dukkan hanyoyin da ake amfani da su wajen tallafa wa ayyukan ‘yan ta’adda a yankin.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]