Sojoji Sun kashe Mayaƙan Boko Haram 3 Tare Da Ceto Mutane 9

Dakarun sojan Najeriya na rundunar, Operation Haɗin Kai sun kashe mayaƙan Boko Haram uku a ƙaramar hukumar Bama dake jihar Borno.

A cewar Zagazola Makama wani masani dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an kashe mayaƙan ne lokacin da sojoji suke gudanar da aikin sintiri.

Ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a ƙauyen Churchur a yayin musayar wuta lokacin da sojojin suke sintiri.

A wani farmakin na daban sojojin sun samu nasarar ceto mutane 9 da suka haɗa da mata uku da ƙananan 6 s sun kuma lalata sansanin mayaƙan na Boko Haram bayan da suka tsere.

Hakan na zuwa ne ƴan kwanaki bayan da sojoji suka kashe wasu mutane uku a wani samame da suka kai maɓoyar Boko Haram da kuma mayaƙan ISWAP a jihohin Borno da Katsina

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...