Dakarun Hedikwatar Brigade ta 14 na Rundunar Sojin Najeriya da ke aiki ƙarƙashin shirin Operation Eastern Sanity II sun kama mutane uku da ake zargi da safarar makamai a ƙaramar hukumar Arochukwu ta jihar Abia.
A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Mazinho Attah, ya fitar, an gudanar da samamen ne da sanyin safiyar ranar bakwai ga watan Yuni bayan samun sahihan bayanan sirri kan yaɗuwar makamai a yankin Amaetiti Iheshiowa.
Sojojin, tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, sun kama Francis Ifere mai shekaru talatin da bakwai, Oso Kalu mai shekaru arba’in da kuma Ifere Oti mai shekaru talatin da biyu.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi bakwai na gida, harsasai masu rai guda ashirin da biyu, babur ɗaya da kuma wata mota da aka ce mai ita ya tsere kafin isowar dakarun.
Rundunar ta ce tana ci gaba da sintiri da sauran ayyukan tsaro a yankunan da ke ƙarƙashinta domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da dakile ayyukan masu aikata laifuka.
Sojoji Sun Kama Mutane Uku Da Ake Zargin Masu Safarar Makamai Ne

