Shugaban kasa Muhammad Buhari ya ce zai iya bakin kokarinsa domin ya tabbatar da cewa yan Najeriya sun zauna lafiya.
Mai magana da yawun shugaban kasar Mallam Garba Shehu shine ya rawaito shugaban kasar na fadin haka lokacin da ya yi bude baki tare da gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari ranar Lahadi a birnin Makka dake ƙasar Saudiyya.
Ya yin buda bakin gwamnan na tare da Sarkin Maradun,Garba Tambari.
Buhari ya tashi daga nan gida Najeriya ranar Alhamis domin aikin Umrah a kasar Saudiyya kuma ana sa ran dawowarsa gida ranar Talata.
A tabakin Garba Shehu shugaban ya bayyana damuwarsa kan asarar rayuka da ta dukiya da ake samu a Zamfara.
nagana da gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz