Shin ka san wane ne marigayi Justice Mamman Nasir?

FACEBOOK/AMINU GAMAWA

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/AMINU GAMAWA

An haifi Justice Mamman Nasir a jihar Katsina a shekarar 1929.

Ya yi karatun sakandare dinsa a Kwalejin Kaduna inda ya samu takardar shaidar kammala karanun sakandare ta WAEC a 1947.

Daga bisani ya tafi jami’ar Ibadan inda ya samu digiri a harshen Latin.

Daga nan kuma ya tafi makarantar horar da lauyoyi inda ya samu digiri a bangaren shari’a a 1956 kuma a wannan shekarar ce aka rantsar da shi a matsayin cikakken lauya a wata kotu da ke Ingila da ake yi wa lakabi da ‘Licoln Inn.”

Ya dawo Najeriya a 1956 a matsayin lauya mai shigar da kara.

A 1961, an nada shi Ministan Shari’a na Arewacin Najeriya inda ya shafe shekaru biyar kan mukamin sai kuma daga baya ya zama darakta a ofishin lauyoyi masu shigar da kara na arewacin Najeriya a 1967.

A 1967 din dai Mamman Nasir ya zama babban lauya a ma’aikatar shari’a a jihar arewa ta tsakiya a wancan lokaci.

Ya rike wannan mukamin na shekaru bakwai inda daga nan ne aka nada shi alkalin kotun koli a 1975.

An kuma nada shi a matsayin shugaban kotun daukaka kara, mukamin da ya rike kenan har zuwa 1992 inda daga nan ne ya zama Galadiman Katsina.

An nada shi a matsayin Galadiman Katsina a ranar 9 ga watan Mayun 19992.

Ya kuma rasu ranar Asabar 13 ga watan Afrailun 2019.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...