Sheikh Kabiru Gombe ya sha da kyar a Kaduna

Rahotanni daga Tudun wadan Kaduna na cewa shahararren malamin Izalar nan da yayi suna wajen wa’azin sunnah Sheikh Kabiru Haruna Gombe ya sha dakyar a wajen wasu fusatattun ‘yan Darikar Tijjaniya dake Tudun Wada Kaduna.

Shedun gani da ido sun tabbatarwa wakilin mu cewa lamarin ya farune da yamma a daidai lokacin da shehin malamin ke gabatar da Tafsirin sa a masallacin ‘yan Lilo dake unguwar Tudun Wada Kaduna.

Wasu fusatattun matasan suka nufi malamin musuluncin dauke da sanduna da sauran muggan makamai a hannun su, sai dai kuma dakyar jami’an tsaron ‘yan sanda da Civil defence da ‘yan kato da gora suka taushi matasan su hana su karasawa jikin malamin.

Da yake zantawa da wakilin mu, wani daga cikin jami’an tsaron ‘yan sandan wajen da al’amarin ya faru, ya ce: “Da Allah bai sa jami’an tsaro na wajen ba da an ji mummunan labari domin matasan sun matukar fusata da yadda suka ce Kabiru Gombe tunda ya fara Tafsirin sa na wannan shekarar babu abinda yake karantarwa sai kiran sunan malamin su Sheikh Dahiru Usman Bauchi yana kafirta shi.”

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...