Sarki Salman bin Abdul’azeez al-Sa’ud ya yi amfani da taron koli na gaggawa na kasashen gabas ta tsakiya dan tattauna batun rikicinsu da Iran.
A jawabin bude taron da aka yi a birnin Makka, sarki Salman ya yi kira ga kasashen duniya su hadu dan hana Iran abin da ya kira tallafawa ‘yan ta’adda da tsoma baki a harkokin kasashe.
Ya kara da zargin Iran dai wa jiragen dakon man Saudiyya hari a baya-bayan nan, zargin da Tehran ta musanta.
Yawancin kasashen yankin Gulf sun rattaba hannun marawa Saudiyya baya, ya yin da makofciyar Iran kuma aminiyarta Iraq ta ki amincewa da hakan tare da cewa bai kamata a karya tsaron kasar ba.