SARS a Najeriya : Majalisar wakilai na son a rika biyan wadanda jami’an SARS suka ci zarafi diyya

'Yan sandan SARS

Shugaban majalisar wakilan Najeriya ya buÆ™aci babban sufeton ‘yan sandan Æ™asar ya É“ullo da wata hanya ta gano duk wani É—an Najeriya da ‘yan sanda suka azabtar don tabbatar da biyansu diyya.

Femi Gbajabiamila, ya ce matakin wani É“angare ne na Æ™oÆ™arin da hukumomi ke yi don kawo Æ™arshen zanga-zangar nuna adawa da zaluncin ‘yan sanda a Nijeriya.

Duk da rushe sashen ‘yan sandan SARS da ya yi Æ™aurin suna, masu zanga-zangar sun ci gaba da jerin gwano har a jiya Talata, lokacin da aka sanar da kafa sabuwar rundunar SWAT don maye gurbin SARS.

Biyan fansa ga wadanda suka mutu ko suka tagayyara sakamakon azabtarwar ‘yan sandan, na daga cikin bukatun masu zanga-zangar neman kawo karshen cin zarafin jama’a da ake zargin ‘yan sandan da yi.

A cewar kakakin, majalisar ta cimma matsayar sanyaya rayukan iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hannun ‘yan sandan kasar ta hanyar biyansu diyya.

Femi Gbajabiamila, ya ce majalisar zata karbi jerin sunayen mutanen tare da yin tanadin biyan iyalansu diyyar a cikin kasafin kudin shekarar 2021.

Honourable Ahmad Sarkin Fulani, dan majalisar wakilai ne daga jihar Zamfara ya kuma shaida wa BBC cewa, dukkan wasu bayanai na wadanda ‘yan sandan suka kashe wasu na gaban kotu, wasu kuma na gaban irin wuraren da ake kai wannan koke.

Ya ce,”Saboda haka, ba za a samu wahalar samun irin wadannan mutane ba da kuma tantance su sannan ayi abin da ya dace ma’ana a bawa iyalansu hakkinsu”.

Dan majalisar ya ce su kansu wadanda aka dauka a matsayin jami’an tsaro, suma mutane ne suna da nasu hakkin wadanda za a duba.

A wani labarin kuma, majalisar wakilan ta bukaci da a kafa ata hukuma mai zaman kanta da zata sanya idanu kan yadda za a gudanar da bincike tare da hukunta duka jami’an ‘yan sandan na SARS da aka samu da laifin aikata irin wannan zalunci kan wadanda suke kamawa.

Wannan matakin na majalisar, kari ne a kan irin matakan da gwamnati ta dauka na rusa rundunar ‘yan sandan ta SARS, da kuma alkawarin yin gyara ga hukumomin tsaron kasar.

Abin tambaya anan, shin ko wadannan matakai da aka dauka zasu iya kashe wutar zanga-zangar kin jinin ‘yan sanda da ke ci gaba da bazuwa zuwa wurare daban-daban na Najeriyar?

Matashiya

‘Yan Æ™asar dai suna zargin rundunar ta SARS da azabtarwa da kisa ba bisa Æ™a’ida ba da saÉ“a dokokin aiki.

A baya dai gwamnatin ƙasar ta ce ba za ta soke rundunar ba, sai dai ta yi mata sauyi ko kuma kwaskwarima kan yadda rundunar ta ke gudanar da ayyukanta, inda ko a kwanakin baya sai da Shugaban Majalisar Dattawan ƙasar Ahmed Lawan ya ce ba zai yiwu a soke rundunar ba sai dai a sauya tsarinta.

A ranar 11 ga watan Oktoban, 2020 ne babban Sifeton ‘Yan Sandan Najeriya Mohammed Adamu, ya soke rundunar da ke yaÆ™i da fashi da makami a Najeriya wato SARS.

Soke rundunar ya biyo bayan jerin zanga-zangar da aka ɗauki kwanaki ana yi a wasu jihohin ƙasar, inda ko a yau Lahadi sai da aka yi irin wannan zanga-zangar a Ingila.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...