Sarki Salman na Saudiyya ya kori ‘yan gidan sarautar daga muƙamansu

Crown Prince Mohammed bin Salman

Bayanan hoto,
Ana yi wa Yarima Mai Jiran Gado Mohammed bin Salman kallon shugaban Saudiyya

An kori jami’an kasar Saudiyya da dama, ciki har da iyalan gidan sarauta guda biyu.

Wata sanarwa ta bayyana cewa Sarki Salman ya sauke Yarima Fahad bin Turki daga kan mukaminsa na kwamandan hadakar dakarun tsaron kasar da ke jagorantar yakin da ake yi a Yemen.

Kazalika an sauke dansa, Abdulaziz bin Fahad, daga mukamin mataimakin gwamna.

Mutanen biyu, tare da karin mutum hudu, suna fuskantar bincike bisa “zargin wadaƙa da kudi” a Ma’aikatar Tsaron kasar.

Yarima Mai Jiran Gadon Sarautar Saudiyya Mohammed bin Salman, wanda shi ne dan sarkin kuma ake yi masa kallo a matsayin mutumin da zai gaji Sarki Salman, yana jagorantar yaki da cin hanci da ake zargin ana aikatawa a gwamnati.

Sai dai masu suka na cewa yana yin hakan ne da zummar kawar da mutanen da ka iya yi masa zagon-kasa a yunkurinsa na zama sarki.

A farkon wannan shekarar, mujallar Wall Street Journal ta ruwaito cewa an kama manyan shugabannin gidan sarautar kasar guda uku, cikinsu har da kanin sarkin, Yarima Ahmed bin Abdulaziz da kuma tsohon Yarima mai jiran gado Mohammed bin Nayef.

Babban abin da ya ja hankalin duniya kan yaki da cin hanci a Saudiyya shi ne kamen da aka yi wa wasu fitattun ‘yan gidan sarautar kasar, ciki har da ministoci da ‘yan kasuwa, inda aka tsare su a shahararren otal din nan na Ritz-Carlton da ke Riyadh a 2017.

An saki galibinsu daga bisani, kodayake sai da suka bayar da dala biliyan 106.7.

Yarima Mai Jiran Gado Mohammed bin Salman mai shekara 35, ya sha yabo daga kasashen duniya a 2016 lokacin da ya yi alkawarin kawo sauye-sauye a fannin tattalin arziki da zamantakewa a kasar da ke da wuyar sha’ani.

Sai dai ya rika shan suka kan batutuwa da dama, ciki har da kisan dan jaridar Saudiyya Jamal Khashoggi a ofishin jakadancin kasar da ke Istanbul na Turkiyya.

More News

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴanbindiga sun hallaka wani shugaban APC a Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Bako Bala, shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Suru a jihar Kebbi, a yayin wani yunkurin yin garkuwa da...

Kotu ta hana VIO kamawa, tsare motoci ko cin tarar direbobi a kan hanya

Justis Evelyn Maha ta Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da umarni da ya hana Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa, wanda aka...

Sojojin Najeriya sun hallaka masu haramtacciyar harƙar man fetur

Dakarun runduna ta 6 ta sojojin Najeriya sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin barayin man fetur ne, tare da cafke wasu 18...