Wanda ya taba lashe kofin duniya a tawagar kwallon kafar Jamus, Sami Khedira ya sanar zai yi ritaya a wasan karshe da Hertha Berling za ta buga ranar Asabar.
Mai shekara 34 ya yanke wannan shawarar, bayan wata uku da ya koma taka leda a Hertha daga Juventus wadda ya lashe Serie A biyar a kungiyar.
Ya lashe kofi 14 jumulla a kungiyoyin da ya buga wa kwallon kafa har da Champions League da La Liga da ya ci a Real Madrid da Bundesliga a Stuttgart.
Khedira ya yi jinyar tiyata da aka yi masa kan karancin bugun zuciya a Juventus a 2019, daga baya ya koma taka leda ya kuma lashe kofi biyu a Italiya daga nan ya je Jamus.
Khedira zai yi ritaya ne mako guda da ta tabbata cewar Hertha za ta ci gaba da buga Bundesliga a badi, bayan da ta tashi ba ci da Cologne a ranar Asabar da ta gabata.
Ya yi wa Hertha wasa takwas, kuma na karshe da zai buga wa kungiyar shi ne ranar Asabar da Hoffenheim a gasar Bundesliga na karshe a kakar bana.