Samar Da Dakarun Tsaron Daji Zai Magance Matsalar Tsaron Najeriya

Wata sanarwar gwamnati ta ruwaito gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje na cewa tuni gwamnati ta kafa kwamiti na musamman da ya kunshi kwararru da dukkanin masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar da aka sanya a gaba.

Wannan mataki dai na kidayar Fulani a Kano na zuwa ne makonni kalilan bayan da rundunar ‘yan sandan jihar ta bullo da tsarin hana Fulani shiga jihar Kano ba tare da takardar shaida ba, a cewar kwamishinan ‘yan sanda Sama’ila Dikko.

Ko da yake, gwamnati na daukar irin wadannan matakai, amma daga cikin masana lamuran tsaro akwai masu ra’ayin cewa samar da dakarun tsaron daji da ake kira “Forest Marshall” ne kawai ka iya kawo karshen fitinar ‘yan ta’adda a Najeriya.

Hakan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da rundunar sojojin ruwa ta Najeriya ke bayyana aniyyar kafa kwalejin horas da Jami’anta a Kano.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...