Ana ta suka da caccakar shugaban kasar Afghanistan, Ashraf Ghani a kan amincewa da ya yi a saki fursunonin yaki yawanci ‘yan kungiyar Taliban a matsayin wata karramawa ta albarkacin Idin karamar sallah.
Shugaban wanda wa’adinsa a matsayin shugaban kasa ya kare a watan da ya wuce, ya bayyana matakin ne a ranar Talata, sai dai bai fadi su waye fursunonin ba da kuma irin laifukansu ba.
Da yake bayar da cikakken bayani game da wannan shiri na afuwa ga ‘yan sarkar, Shugaban na Afghanistan, Ashraf Ghani, ya ce matakin na daga cikin abubuwan da suka amince a zaman tattaunawa na tabbatar da zaman lafiya wanda aka shirya yi da kungiyar Taliban.
To sai dai wannan mataki na gwamnatin na sasantawa da wanzar da zaman lafiya da masu tayar da kayar bayan, albarkacin Idin, ya haifar da takaddama tare da cin karo da suka tun daga bayyana shi, abin da ya sa ake ta kira da gwamnatin ta yi watsi da shi.
Masu nuna shakku ko tababa da dari-dari, da kuma masu suka a game da dabarar, suna nuna cewa su kam ba su ga dalilin sakin mayakan ba, alhalin kungiyar ‘yan Taliban din na ci gaba da kai hare-hare.
‘Yan takarar shugabancin kasar da dama, na cewa Mista Ghani ba shi ne shugaban Afghanistan ba na halaliya a yanzu, saboda haka babu wani dalili ko iko da yake da shi da zai aiwatar da wani muhimmi ko babban hukunci kamar wannan.
Sai dai Mista Ghani, ya kafe a kan ra’ayinsa na ci gaba da zama a kan mulki, har sai an yi sabbin zabuka, amma kuma ‘yan hamayya sun ce atafau hakan ba za ta sabu ba.
A kan hakan sun yi barazanar bijirewa tare da yin gargadin tayar da zaune tsaye a siyasar kasar ta Afghanistan, idan ya ci gaba da zama a kan mulki.