Sa’idu Alkali Ya Janye Daga Takarar Gwamnan Gombe Ta APC



Tsohon ministan sufuri kuma ɗan takarar gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar APC, Sanata Sa’idu Ahmed Alkali, ya sanar da janye kansa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da za a gudanar ranar 21 ga watan Mayun 2026.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan yaɗa labarai, Umar Alkali Jibrin, ya fitar, Sanata Alƙali ya danganta matakin da zargin rashin gaskiya da karya dokokin zaɓe a cikin tsarin fidda gwani na jam’iyyar a jihar.

Ya bayyana cewa duk da cika sharuddan shiga takara da kuma wuce tantancewar jam’iyyar, yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na wasu kujerun majalisa da sanatoci ya sa ya rasa amincewa da sahihancin tsarin.

A cewarsa, an gudanar da zaɓukan cikin maguɗi da rashin adalci, tare da karya sashe na 86 na dokar zaɓe ta 2026.

Sai dai duk da janyewar tasa daga takarar, Sanata Alƙali ya tabbatar da ci gaba da goyon bayansa ga jam’iyyar APC domin samun nasara a zaɓen shekarar 2027.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]