Rundunar Sojin Saman Najeriya Ta ce Ta Sami Gagarumar Nasara a Yakin Da Take Yi Da ‘Yan Ta’adda A Sokoto | VOA Hausa

A daidai lokacin da Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta sami gagarumar nasarori a yakin da take yi da ‘yan ta’adda a yankin gabashin jihar Sokoto, mazauna yankunan sun ce har yanzu ba za’a rasa fargaba ba, domin ‘yan bindigar suna nan kusa da jama’ar yankin.

Babban hafsan sojin saman Najeriya, Air marshall Sadiq Baba Abubakar shi ne ya furta batun samun nasarar a wurin bikin da rundunar sojin sama da ke jihar Sokoton ta gudanar don taya murnar Sallah ga sojojin da ke bakin daga a yankin.

Air marshall Sadiq Baba Abubakar, ta bakin kwamandan rundunar dabarun kai farmaki da jirage, AVM Olusegun Philip ya ce, aikin da mayakan saman suke gudanar wa ya taikamaka gaya wajen dakile ayukan ta’addanci a yankunan.

Wasu daga cikin mazauna yankunan sun shaidawa wakilin muryar Amurka cewa, sun gudanar da bikin sallah lafiya, ba tare da wani tashin hankali ba. Amma sun nuna damuwarsu da fargaba, domin a cewar su ‘yan bindigar suna kusa da yankunan nasu.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...