Mai horas wa Gernot Rohr bai ce komai ba kan makomarsa a matsayin kocin Najeriya, bayan rade-radin lattin biyan albashi.
Mai shekara 66 dan kasar Jamus wanda yarjerjeniyarsa zai kare a Yunin 2022, bai karbar albashinsa a kan lokaci, tun da ya fara jan ragamar Super Eagles a watan Agustan 2016.
Hukumar kwallon kafar Najeriya, NFF ta ce kocin na bin albashin watan Satumba ne kadaui, ba watanni uku ba kamar yadda rahotanni ke cewa.
Wasu rahotannin na cewar Rohr zai ja ragamar Super Eagles wasansa na karshe a wasan sada zumunta da Brazil a Singapore.
Tawagar kwakllon kafar Brazil da ta Najeria sun tashi 1-1 a wasan sada zumunta da suka yi, karo na biyu da suka fafata tun 2003, inda Brazil ta ci 3-0 a Abuja.
Tun kan nan Brazil ta buga 1-1 da Senegal ranar Alhamis 10 ga watan Oktoba a Singapore, a karawar ce Neymay ya buga wa Brazil wasa na 100.
Tsohon kocin tawagar Gabon da Niger da Burkina Faso ya kai Najeriya gasar cin kofin duniya da aka yi a Rasha, wanda Super Eagles ta kasa kai wa karawar zagaye na biyu.
Haka kuma Rohr ya kai gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a Masar, wanda Super Eagles ce ta yi ta uku a wasannin.