Rashin kayan aiki yana kawo wa yaƙi da rashin tsaro cikas a Abuja—Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, a ranar Litinin ya bayyana cewa rashin isassun kayan aiki da motocin aiki na kawo cikas wajen yaki da ‘yan fashi da garkuwa da mutane a babban birnin tarayya Abuja.

Wike, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, ya kuma dora laifin yawaitar sace-sacen mutane a wasu al’ummomin da ke kan iyaka na babban birnin tarayya Abuja da rashin kayan aiki da za a yi amfani da su wajen gano masu aikata laifuka.

Sai dai ya tabbatar wa mazauna yankin cewa nan ba da dadewa ba za a magance matsalolin tsaro bayan amincewar da shugaba Bola Tinubu ya yi na sayo kayan aiki na gaggawa.

Ya ce an amince da sayo kayan aikin bin diddigi da motocin aiki don taimakawa wajen gano masu garkuwa da mutane.”

More News

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Majalisar dokokin Zamfara ta tsige kakakinta saboda tsanantar rashin tsaro a jihar

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige kakakinta, Bilyaminu Moriki, tare da nada Bashar Gummi, a matsayin kakakin majalisar. Hakan ya biyo bayan kudirin da dan...

Ƴan bindiga sun kashe mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da kisan mutane shida da wasu ‘yan bindiga suka yi a karamar hukumar Faskari a jihar. Jami’in hulda...

Sace-sacen motoci ya yawaita a Adamawa—Ƴan sanda

Ana ci gaba da samun karuwar sace-sacen motoci a jihar Adamawa, kamar yadda rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar. Rundunar ‘yan sandan ta bayyana haka...