PDP ta gaza cimma matsaya kan jiga-jiganta bakwai da suka yi murabus | BBC Hausa

Uche Secondus

Asalin hoton, PDP

Kwamitin amintattu na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya PDP, ya kammala wani zama da ya yi ba tare da cimma matsaya ba a kan murabus din da wadansu mataimaka ga Æ´an kwamitin gudanarwar jam’iyyar su bakawai suka yi.

A taron da kwamitin ya gudanar a ranar Alhamis ya ce zai sake wani zama inda yake sa ran samun mafita.

Jam’iyyar PDP na fama da rikicin gida, har wasu na kira ga shugaban jam’iyyar na Æ™asa Uche Secondus ya sauka daga muÆ™aminsa.

Bayan shafe fiye da sa’a uku suna tattaunawar sirri, haka Æ´an kwamitin suka tashi ba tare da yanke wata shawara a kan waÉ—ansu manyan rigingimun cikin gida da suke addabar jam’iyyar ba.

Batun masu sauya sheÆ™a daga PDP zuwa wata jam’iyyar, da na wasu mataimaka ga Æ´an kwamitin gudanarwa su bakwai da suka fusata suka yi murabus daga muÆ™amansu na daga cikin manyan batutuwan da aka gaza cimma matsayar a kansu.

Masu murabus É—in na zargin shugaban jam’iyyar na Æ™asa, Mista Secondus da rashin kamanta gaskiya wajen sarrafa kuÉ—aÉ—en jam’iyyar, amma ya musanta.

Ko da yake, wasu Æ´an jam’iyyar na zargin cewa masu sauka daga muÆ™aman nasu da zama karnukan farautar wasu Æ™usoshin a PDP, waÉ—anda ke amfani da su wajen ganin sun kai Mista Secondus Æ™asa.

Wasu Æ´an kwamitin dai na da ra’ayin cewa ya kamata a bi tanadin da kundin mulkin jam’iyya ya yi na hanyoyin sasanta rikici, ta yadda za a yi sulhu baki-alaikum, da ya haÉ—a da rarrashi ko ban-baki, idan kuma ta Æ™iya… sai a kai ga matakan ladabtarwa.

Amma bayan zaman, shugaban kwamitin amintattun jam’iyyar PDPn, Sanata Walid Jibril ya ce ba a kai ga cim ma maslaha ba.

“Muna nan za mu ci gaba da magana, ba mu gama meeting É—in ba. Ba a cimma matsaya ba ne kawai.

“Maganar fitcewar mutane kuwa kan faru ga kowace jam’iyya. Don haka abin da ya kamata a yi shi ne a zauna a yi magana.

“A gaya mana dalilin tafiyar ba wai a dinga fita hakan nan ba dalili ba,” a cewar Sanata Walid.

Burin tsige Mista Secondus

Asalin hoton, PDP

Bayanan hoto,
A baya-bayan nan ma gwamnonin PDP sun yi ƙorafi kan yadda APC ta mayar da fadar shugaban Najeriya wajen karɓar waɗanda suka sauya sheƙa

Bayan masu murabus daga PDP, akwai wasu da ba su É“oye maitarsu ba, ta rashin goyon bayan cewa Mista Secondus ya ci gaba da jagorantar jam’iyyar, musamman irin su gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, wanda a wani lokaci har sukan yi sa-in-sa da juna.

Sannan akwai masu ra’ayin ya kamata a bar Secondus din ya kammala ragowar wata uku ta wa’adin mulkinsa, suna cewa bai kamata a tunkari babban zaben 2023 da rikicin shugabanci ba.

Yayin da wasu ke so a sabunta masa wa’adi, wasu kuma cewa suke lallai a tilasta masa yin murabus, saboda zamansa a kan karagar na da haÉ—ari.

Ibrahim Isa na BBC Hausa ya tuntuɓi Senata Walid Jibril ko da wani tartibin matakin da suka dauka a kan wannan lamarin?

“Mu ba za mu ce wa wani ya sauka ba a yanzu, ba mu kai lokacin ba tukun. Idan muka fara maganar wani ya sauka a yanzu ba mu yi daidai ba.

“Muna da lokaci da za mu yi wadannan abubuwan tukun ba tare da mun samu matsala ba.

“Amma an samu ci gaba, ko don halartar da Gwamna Wike ya yi,” ya Æ™ara da cewa.

Jam’iyyar PDPn dai tana Æ™oÆ™arin farfaÉ—owa ne daga kaÉ—uwar da ta yi sakamakon rashin wasu gwamnoni uku da ta yi, da wasu manyan Æ´aÆ´anta da jam’iyya mai mulki ke mata É—auki É—ai-É—ai.

Ana haka kuma sai ga wannan guguwar masu murabus ta kaÉ—a, har ana maganar raba shugaban jam’iyyar da rawaninsa.

A gefe guda kuma ga wasu jihohi tara da ba su samu yin tarukan jam’iyyar ba amma Æ´an kwamitin amintattun sun ce za su sake zama.

Sun kuma ce suna da yaÆ™inin cewa nan da makon gobe za su daidaita kawunan Æ´aÆ´an jam’iyyar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...